Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya, ya buƙaci ‘yan ƙasarsa da su zauna cikin shirin ko-ta-kwana kan yiwuwar samun zanga-zanga da kuma takaita zirga-zirga a ranar 25 ga watan Febrairu da kuma 11 ga watan Maris.
A wata sanarwa da ofishin jakadancin ya fitar a shafinsa, ya kuma shawarci ‘yan ƙasar da ke Najeriya da su guji shiga tarukan jama’a saboda za su iya rikiɗewa zuwa tarzoma.
Ofishin ya kuma shawarci ‘yan ƙasarsa da su tanadi isashen abinci da kuma ruwa a gidajensu ko da za a ƙara takaita zirga-zirga har bayan ranakun zaɓe. In ji BBC.
Sauran shawarwarin da ofishin ya bai wa ‘yan ƙasar ta Amurka da ke Najeriya sun haɗa da:
- Tanadar abinci da ruwa na tsawon kwanaki uku
- Samar da jakar da za ta kunshi takardun tafiye-tafiye da magani da kudi da kuma tufafi, ko da yiwuwar mutum zai iya sauya wajen zama.
- A guji shiga tarukan jama’a.
- A tanadi takardar shaida.
- Zama cikin shirin ko-ta-kwana.
- A tabbata wayar salula na da caji.
- A kuma bibiyi labaran kafafen yaɗa labarai don sanin abin da ke faruwa.