Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe iyakokin ƙasar nan sa’a 24, gabanin babban zaɓen ƙasa da ke tafe a ranar Asabar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Hukumar Shige da Fice ta Najeriya ta fitar a shafinta na twita wanda ya samu sa hannun shugabanta, Isah Jere Idris.
Sanarwar ta ce daga gobe Asabar za a rufe dukkan iyakokin ƙasar na ƙasa har zuwa ranar Lahadi 26 ga watan Febrairun 2023.
Idris Jere ya buƙaci dukkan shugabannin hukumar da ke kan iyakoki da su tabbata an bi sahun wannan umarni.
Ya ce hukumar a shirye take wajen ganin ta bayar da gudummawa na ganin an gudanar da zaɓukan ƙasar lami lafiya.