fidelitybank

Zaben 2023: A guji kalaman tunzuri – ‘Yan Sanda

Date:

Gargaɗin na zuwa ne bayan da ake ta samun rahotonnin tashe-tashen hankula a wasu sassan ƙasar sakamakon matsalar ƙarancin takardun sabbin kuɗin ƙasar.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar ta hannun jami’inta na hulda da jama’a Olumuyiwa Adejobi, rundunar ta ce kiran ya zama wajibi yayin ya rundunar ke samun bayanai game da yadda wasu ke mayar da martani tare da furta kalaman da za su iya janyo tashin hankali a ƙasar.

Sanarwar ta ce mutanen kan yi kalaman – da za su iya tunzura jama’a domin aikata wasu abubuwan da suka saɓa wa doka – domin cimma wata manufarsu.

A dan haka ne rundunar ke kira ga ‘yan ƙasar da su kwantar da hankulansu, su kuma rugumi zaman lafiya a yayin da gwamnati tarayya ta tabbatar da cewa tana ɗaukar matakan da suka dace wajen magance matsalar ƙarancin kudi da na man fetur tare da daidaita al’amura.

Haka kuma sanarwar ta yi kira ga ‘yan ƙasar da su kauce wa duk wani abu da zai tayar da ruɗani da lalata dukikyoyin gwamnati da duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaɓen ƙasar da ke tafe.

Rundunar ‘yan sandan ta ce tana aiki da sauran hukumomin tsaro da na tattara bayanan sirri domin tabbatar da zaman lafiya, don gudanar da harkoki cikin kwanciyar hankali.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp