fidelitybank

Zaben 2023: A guji kalaman tunzuri – ‘Yan Sanda

Date:

Gargaɗin na zuwa ne bayan da ake ta samun rahotonnin tashe-tashen hankula a wasu sassan ƙasar sakamakon matsalar ƙarancin takardun sabbin kuɗin ƙasar.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar ta hannun jami’inta na hulda da jama’a Olumuyiwa Adejobi, rundunar ta ce kiran ya zama wajibi yayin ya rundunar ke samun bayanai game da yadda wasu ke mayar da martani tare da furta kalaman da za su iya janyo tashin hankali a ƙasar.

Sanarwar ta ce mutanen kan yi kalaman – da za su iya tunzura jama’a domin aikata wasu abubuwan da suka saɓa wa doka – domin cimma wata manufarsu.

A dan haka ne rundunar ke kira ga ‘yan ƙasar da su kwantar da hankulansu, su kuma rugumi zaman lafiya a yayin da gwamnati tarayya ta tabbatar da cewa tana ɗaukar matakan da suka dace wajen magance matsalar ƙarancin kudi da na man fetur tare da daidaita al’amura.

Haka kuma sanarwar ta yi kira ga ‘yan ƙasar da su kauce wa duk wani abu da zai tayar da ruɗani da lalata dukikyoyin gwamnati da duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaɓen ƙasar da ke tafe.

Rundunar ‘yan sandan ta ce tana aiki da sauran hukumomin tsaro da na tattara bayanan sirri domin tabbatar da zaman lafiya, don gudanar da harkoki cikin kwanciyar hankali.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp