Mutumin da ake ganin shi zai zama shugaban gwamnatin Jamus nan ba da jimawa ba ya ce abu muhimmi da zai mayar da hankali a kai shi ne hadin kan ƙasashen Turai.
Friedrich Merz ya ce suna buƙatar hakan ne domin rage dogaro kan Amurka, wadda ya ce ta “daina damuwa da makomar nahiyar Turai”.
Mista Merz ya ce dole ne Turawan su dogara da kansu, yana mai dasa ayar tambaya kan makomar kungiyar tsaro ta NATO.
Ya kuma nuna fushi da sukar matakin jam’ian Amurka na tsoma baki a harkokin Jamus bayan Elun Musk ya bayyana goyon baya ga jam’iiyar adawa ta AFD.