Shugaba Xi Jinping na China ya yi alƙawarin zuba jarin sama da dala biliyan 50 kan ayyuka da dama a Afirka cikin shekaru uku masu zuwa, ciki har da samar da ayyukan yi.
Yayain da yake jawabi a babban taron ƙolin tsakanin China da Afirka, Shugaba Xi ya ce kyakkyawar alaka tsakanin ƙasarsa da Afirka na da tarihi mai tsawo.
Ya ƙara da cewa a shirye China ta ke ta ƙara sanya hannu a fannonin more rayuwa da makamashi da cinikayya a nahiyar Afirka.
Shugabannin Afirka fiye da 50 da babban magatakardar Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres ne ke halartar taron.