Shugaban gwamnatin riƙon ƙwaryar Syria, Ahmed Al-Sharaa ya ce gwamnatinsa za ta farauto sirarun mutanen da har yanzu ke nuna goyon baya ga hamɓararren shugaban ƙasar, Bashar Al-assad, domin su fuskanci shari’a bayan shafe kwana biyu ana rikici a yankin Latakia.
Al-Sharaa ya ce waɗanda suka aikata kisa kan fararen hular da ba su ji ba su gani ba za su fuskanci hukunci.
Wata ƙungiya da ke sanya idanu kan yaƙin Syria ta zargi dakarun gwamnati da aikata kisan fareren hula fiye da 160 a yankin da ke gaɓar teku.
Wani mai fafutika a yankin na Latakia ya faɗa wa BBC cewa, mayaƙan da ke goyon bayan gwamnati sun aikata kisan ba sani ba sabo a ƙauyukan da tsiraru ƴan ƙabilar Assad ta Alawi ke zama,