fidelitybank

Za mu yi karin farashin Burodi a watan Yuli – Kungiya

Date:

Ƙungiyar masu gidajen burodi ta kasa, ta ce, za ta ƙara farashin burodi da kashi 15 cikin ɗari daga ranar 24 ga watan Yuli.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, bayan kammala taron shugabanninta na ƙasa, ƙungiyar ta ‘Association of Master Bakers and Caterers of Nigeria’ ta ce ta ɗauki matakin ne bayan la’akari da nunnukawar farashin kayan aiki.

Sanarwar wadda ta samu sa hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa, Alhaji Mansur Umar ta ce tashin farashin ya biyo bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin Tarayya ta yi.

A ranar 29 ga watan Mayun 2023 ne shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur a cikin jawabinsa na karɓar mulki.

Lamarin ya haifar da tashin litar man fetur daga kimanin naira 200 zuwa sama da naira 500 a faɗin ƙasar, wani abu da ya haifar da tashin farashin sufuri da kayan masarufi.

Ƙungiyar ta ce abubuwan da take amfani da su wajen gudanar da sana’ar, waɗanda suka haɗa da man fetur, da gas, da fulawa, da suga da sauran su duk sun yi tashin gwauron zabi.

Haka nan ƙungiyar ta koka kan yadda hukumomi daban-daban a ƙasar ke karɓar haraji, kala-kala, wani abu da ke ƙara saka masu gidajen burodin cikin matsi.

Kan haka ne ta ce “An umurci dukkanin shugabannin ƙungiyar na yanki su tabbatar cewa ƴaƴan ƙungiyar sun bi wannan umarni, har sai idan sun samu wani sabon umarnin daga uwar ƙungiyar ta ƙasa.”

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp