fidelitybank

Za mu yi jana’izar Sojoji 17 da aka kashe mana a Delta – Sojoji

Date:

Rundunar sojin ƙasar nan ta sanar da yau 27 ga watan Maris a matsayin ranar da za a yi jana’izar sojoji 17 da aka kashe a garin Okuama da ke jihar Delta.

Rundunar ta ce za a yi jana’izar ne a maƙabartar sojoji ta ƙasa da ƙarfe 3 na yamma.

Hakan yazo ne ƴan makonni bayan wasu ɓatagari sun kashe wasu daga cikin sojojin da ke aiki ƙarƙashin runduna ta 181 da aka turo domin kwantar da tarzomar da ke tsakanin al’ummar garin Okuama da Okoloba na jihar.

Shugaban ƙasa Bola Tinibu da ƴan Najeriya da dama sun yi allahwadai da kisan sojojin.

Shugaban ƙasa ya umarci rundunar da ta tabbatar cewa waɗanda suka aikata kisan sun fuskanci hukunci. A hoton da rundunar sojin Najeriya ta wallafa a shafinta na X, sojojin da aka kashe sun haɗa da :

  • Lt Col AH Ali, kwamandan runduna ta 181
  • Manjo SD Shafa
  • Manjo DE Obi
  • Kyaftin U Zakari
  • Staff Sajant Yahaya Saidu
  • Koporal Yahaya Danbaba
  • Koporal Kabiru Bashir
  • Lance Koporal Bulus Haruna
  • Lance Koporal Sole Opeyemi
  • Lance Koporal Bello Anas
  • Lance Koporal Hamman Peter
  • Lance Koporal Ibrahim Abdullahi
  • Private Alhaji Isah
  • Private Clement Francis
  • Private Abubakar Ali
  • Private Ibrahim Adamu
  • Private Adamu Ibrahim

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp