Kwamitin majalisar dattawa mai kula da al’amuran zaɓe, ya ce zai tursasa wa hukumar zaɓe mai zaman kanta INEC ta riƙa shigar da sakamakon zabe a intanet.
Shugaban kwamitin, Sanata Sharafadeen Alli, ya shaida wa gidan talabijin na Channels a ranar Talata cewa, dokar da ake bi a yanzu ba ta tilasta wa INEC shigar da sakamakon zabe a kan intanet ba, amma kwamitin na ƙoƙarin gyara dokar.
Baya ga sauran sauye-sauyen da ake yi na gudanar da zabe, Alli ya ce kwamitin ya bayar da shawarar warware duk wasu rikita-rikitar tsayar da ƴan takara kafin zabe da tare kuma da inganta fasahar da ake amfani da ita lokacin zabe, sai kuma magance matsalolin da aka samu a baya na amfani da fasaha a zabuka.