Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa tsakaninta da Birtaniya da Faransa da Jamus a Istanbul kan shirinta na nukiliya.
Kafar yaɗa labaran Iran ta ce ma’aikatar harakokin wajen ƙasar ta tabbatar da cewa Tehran ta amince da tayin tattaunawar da za a yi a ranar Juma’a.
Tattaunawar za ta kasance ta farko tun bayan hare-haren da Isra’ila da Amurka suka kai wa Iran a watan Yuni.
Iran kuma na fuskantar matsin lamba na ta amince ta hau teburin tattaunawa da Amurka.
Shugabannin ƙasashen Turai sun ce za su lafta wa Iran sabbin takunkumai idan har babu ci gaba a yarjejeniyar nukiliyar.