Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya tattauna batutuwan da suka shafi tsaro a yammacin Afirka da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken da ke ziyarar aiki a ƙasashen Afirka hudu.
Blinken ya ce, Amurka ta kuduri aniyar haɗa ƙarfi da ƙarfe kan tsaro da Najeriya” yayin da ƙasashen biyu ke yaƙi da masu iƙirarin jihadi a yankin.
Najeriya ta kuma sha fama da tashe-tashen hankula a arewaci da kuma babban birnin tarayya Abuja, inda wasu gungun ‘yan bindiga suka addabi al’umma tare da yin garkuwa da jama’a domin neman kuɗin fansa.
Ƙasashe a yankin Sahel na fuskantar tabarbarewar zaman lafiya, bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a hudu daga cikin mambobi 15 na ƙungiyar Ecowas.
Amurka dai na ci gaba da yunƙurin ganin ta ci gaba da yin tasiri a nahiyar Afirka, a daidai lokacin da Rasha da China ke fafatawa.