fidelitybank

Za mu taimaka wa Asibitin Maiduguri – Red Cross

Date:

Tawagar Likitoci daga ƙungiyar agaji ta ‘International Committee of the Red Cross (ICRC) za ta tallafa wa likitocin asibitin Maidugiri wajen yi wa mutanen – da harin ƙunar baƙin wake a Gwoza – magani.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta ce tawagar ƙwararrun likitocin nata za ta yi aiki da likitin asibitin koyarwa na birnin Maiduguri wajen ceto rayukan mutanen da harin ya yi musu mummunar illa.

Mutane da dama ne suka samu munanan raunuka a lokacin harin da wasu ‘yan ƙunar baƙin wake suka kai garin Gwoza a ƙarshen mako.

An kai mutum 41 da suka jikkata zuwa asibitin na Maiduguri, da suka haɗa da mata da ƙananan yara a ranarkun Asabar da Lahadi domin ba su kulawar gaggawa.

Ƙungiyar ICRC ta kuma bayar da tallafin magunguna da wasu kayyaki ga asibitin domin taimaka wa ɓangaren kula da masu buƙatar kulawar gaggawa.

Mataimakiyar shugaban tawagar ƙungiyar da suka je Maiduguri, Diana Japaridze ta ce halin da marasa lafiyar ke ciki a asibitin ”abin tayar da hankali ne”.

“Muna kira da babbar murya cewa a yaƙi dole a kare fararen hula musamman mata da ƙananan yara, kuma asibiti wuri ne na ceton rai, ba wurin salwantar da rai ba.”

”Hari kan mai uwa da wabi kan fararen hula, abu ne da ya saɓa wa dokokin duniya, haka ma cibiyoyin kula da lafiya da ma’aikata, su ma dole ne su samu kariya, ba a kai musu hari ba”, in ji ta.

A ranar Asabar ne wasu mata huɗu suka tayar da boma-bomai a wurare daban-daban a Gwoza lokacin da ake tsaka da bikin aure.

Lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum 32 tare da jikkata gommai, kamar yadda mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp