fidelitybank

Za mu tabbata mun yi bincike kan harin ‘Yan Sa Kai da aka kai Zamfara – Sojoji

Date:

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce tana gudanar da bincike kan wasu rahotannin da suka ce an kashe fararen hula a yayin wani harin da aka kai a jihar Zamfara da ke yankin arewa maso yammacin ƙasar a karshen makon da ya gabata.

Wata sanarwa da ta fito daga ofishin darektan sashen hulɗa da jama’a da yaɗa labarai na rundunar, Air Vice Marshal Olusola Akinboyewa, ta ce an kai harin ne kan wasu ƴan bindiga a yankin Tungar Kara da ke ƙaramar hukumar Zurmi a jihar ta Zamfara inda aka yi nasarar kuɓutar da wasu da aka yi garkuwa da su.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, duk da ya ke harin ya yi nasarar tarwatsa wani sansanin ƴanbindiga da suka addabi yankin, rundunar ta nuna matuƙar damuwa kan rahotannin rashin rayukan fararen hula da aka samu inda ta ƙara da cewa tana kan gudanar da bincike kuma za a sanar da sakamakon hakan da zaran ya kammala.

Ta kuma bayar da tabbacin cewa zata ci gaba da ɗaukar matakai da za su tabbatar da cewa an kiyaye rayukan fararen hula a yayin da ta ke ƙokarin tabbatar da ingantaccen tsaro a sassan ƙasar.

A ranar Lahadin da ta gabata ne dai mazauna yankin na Tungar Kara suka ce aƙalla mutane 15 ne suka mutu sakamakon harin sojoin, ciki ma har da ƴan sintirin da ke ƙoƙarin yaƙar ƴanbindigan.

A cikin watan Disamba aƙalla mutane 10 ne suka mutu a lokacin da wani jirgin yaƙin soji ya kai hari bisa kuskure kan wasu fararen hula a jihar Sokoto da ke yankin arewa maso yammacin ƙasar.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp