fidelitybank

Za mu sayar da buhun shinkafa naira dubu 400 – Gwamnati

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, ta karye farashin shinkafa wadda ta tanada da za a sayar a sassan kasar da nufin samar da sauki ga ƴan kasa.

A kasuwa dai ana sayar da shinkafar ne kusan N80,000, ɗaya daga cikin dalilan da suka sa wasu ƴan Najeriya ke shirin gudanar da zanga-zanga domin nuna fushinsu da tsadar rayuwa.

Amma Gwamnatin tarayya ta ce ta karya farashin shinkafar zuwa N40,000 kan duk buhu daya 50kg, kamar yadda ministan yada labarai na kasar Muhammad Idris ya shaida wa BBC.

Ya ce tuni an ware wuraren da za a sayar da shinkafar a sassan jihohin Najeriya. Sai dai gwamnatin ba ta bayyana lokacin da za ta fara sayar da shinkafar mai sauƙin kuɗi ba.

Amma a cewar ministan, karya farashin na zuwa bayan gwamnatin tarayya ta bayar da tirelar shinkafa 20 ga duk jihohin ƙasar domin raba wa ƴan Najeriya.

“Da farko an ba gwamnoni shinkafa su raba wa masu ƙaramin ƙarfi kyauta kuma yanzu gwamnati ta tanadi shinkafa da za ta sayar da rahusa domin samar da sauƙi ga ƴan Najeriya,” in ji ministan.

Ya ce shinkafar da za a sayar a farashi mai rahusa ba wadda gwamnatin tarayya ta raba wa gwamnonin jihohi ba ce.

Shinkafa na ɗaya daga cikin abincin da ake ci a Najeriya, kuma farashinta a kasuwa kusan ya gagari aljihun wasu ƴan ƙasar.

Ministan ya ce gwamnati ta lura da tsadar shinkafar a kasuwa, shi ne ya sa ta ɗauki matakin samar da ita a farashi mai rahusa domin ƴan ƙasa su amfana

Kuma a cewarsa gwamnati ta ɗauki wannan matakin ne domin tabbatar da wadatar abinci a Najeriya.

“Idan aka ci gaba da kawo matakai irin waɗannan, sannu a hankali abubuwa za su yi sauƙi.”

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp