fidelitybank

Za mu sanya ido a kan ‘yan siyasa masu haifar da rikici a Najeriya – Burtaniya

Date:

Burtaniya ta ce, ta zura ido kan ‘yan siyasa da jam’iyyunsu, jami’an tsaro da duk wani mutum da zai haifar ko ingiza rikici ta shafuka sada zumunta gabannin babban zaɓe da ke tafe a 2023 a ƙasar.

Jakadiyar Burtaniya a Najeriya, Catriona Laing ce ta sanar da hakan lokacin ganawa da kwamitin gudanarwa ta harkokin zaɓe na PDP a Abuja.

Ms Laing ta ce zaɓen 2023 na da muhimmanci sosai ga Afirka da duniya baki ɗaya, don haka dole ido na kan Najeriya kuma Burtaniya za ta zura ido sosai a kan ƙasar.

Ta kuma ce Burtaniya ta damu matuƙa kan abubuwan da suka faru na baya-bayanan, ciki harda rikice-rikice 52 da ke da alaƙa da zaɓe a jihohi 22, ciki harda harin da aka kai wa tawagar PDP a Borno.

Ta ce Burtaniya ba za ta goyi-bayan kowacce jam’iyyar siyasa ba, domin tana da burin ganin kowane ɗan kasa ya samu damar zaɓin abin da yake gani shi ne cancanta a gareshi.

Jami’ar ta kuma shaida cewa suna ta tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki harda Inec, da kungiyoyin fararan-hula da ‘yan siyasa domin tabbatar da sahihin zaɓe cikin kwanciyar hankali.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...
X whatsapp