Ministan ƙwadago, Muhammadu Dingyadi, ya ce gwamnatin Tarayya za ta yi aiku tuƙuru domin magance matsalar rashin aikin yi a ƙasar nan.
Da yake magana a gaban kwamitin ƙwadago na majalisar dattawa, ƙarƙashin Sanata Diket Plang, ministan ya bayyana cewa suna ƙoƙari domin yaƙi da rashin aikin yi.
“Muna aiki tuƙuru ba dare ba rana domin yaƙi da rashin aikin yi saboda yana cikin masu matuƙar muhimmanci a gare mu. Dukkan tsare-tsarenmu na koyar da sana’a mun yi su ne domin rage rashin aikin yi,” kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.
A game da ƙididdigar rashin aikin yi na ƙasar, ministan bai bayyana adadi ba, inda ya ce, “muna ƙoƙari domin haɗa alƙaluma.”