Gwamnan jihar Rivers, Siminalaya Fubara ya ce za su yi amfani da hukuncin da kotun ƙoli ta yanke kan sahihancin shugabancin majalisar dokokin jihar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar.
A ranar Juma’a ce kotun ƙolin ta rushe zaɓen ƙananan hukumomin jihar, sannan ta ce tsagin Martin Chike Amaewhule, wanda ke tare da Ministan Abuja, Nyesome Wike ne sahihin shugaban majalisar, inda ta buƙaci babban bankin Najeriya ya dakata da ba jihar kasonta na tarayya har sai gwamnan ya gabatar da kasafi a gaban majalisar.
“Muna bin doka da oda, duk da cewa za mu iya yin kuskure a matsayinmu na ƴan’adam. Kasancewar hukuncin kotu ya rushe zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumominmu, ina umartar dukkansu su miƙa aiki ga shugabannin aikace-aikace na ƙananan hukumomi, waɗanda za su yi riƙo kafin a sake gudanar da sabon zaɓe.”
Ya yi kira ga ƴan jihar su kwantar da hankalinsu, tare da cigaba da gudanar da ayyukansu ba tare da tashin hankali ba.