fidelitybank

Za mu sake yin zanga-zanga a kan kudurin taken Najeriya – TBM

Date:

Kungiyar Take It Back Movement, wata kungiya ce mai fafutukar kare hakkin bil adama a bayan zanga-zangar EndBadGovernance da aka kammala, ta yi barazanar sake gudanar da zanga-zangar a fadin kasar game da kudirin doka mai cike da takaddama kan taken kasar.

Jaridar DAILY POST ta ruwaito cewa a yanzu haka akwai wani kudirin doka da ke neman hukunta ‘yan Najeriya da suka ki rera taken kasar a zauren majalisar wakilai.

Kudirin dokar wanda kakakin majalisar Tajudeen Abbas ke daukar nauyinsa, na neman a ci tarar Naira miliyan 5 ko shekaru 10 a gidan yari ko kuma duka biyun ga duk wanda ya lalata alamomin kasa, ya ki karanta taken kasa da kuma yin alkawari.

Da take mayar da martani, kungiyar Take It Back a wata sanarwa da ta fitar a ranar Larabar da ta gabata ta yi watsi da kudurin dokar, inda ta ce hakan na barazana ga ‘yancin ‘yan Najeriya.

Sanarwar wacce kodinetan kungiyar na kasa, Juwon Sanyaolu ya sanya wa hannu ta ce “ya kamata a yi watsi da kudirin ba a amince da shi ya zama doka ba, a’a, ya kamata gwamnati ta mayar da kokarinsu wajen magance matsalolin da ke haifar da rashin jituwa da rigingimu a kasarmu. “.

Sun yi barazanar gudanar da zanga-zanga a fadin kasar idan har dokar ta zama doka duk da nuna fushin da jama’a suka yi.

Wani bangare na sanarwar ya kara da cewa, “A matsayin kungiyar masu goyon bayan jama’a da suka sadaukar da kansu don tabbatar da adalci da ci gaba, mun lura da yadda jama’a ke mayar da martani ga kudirin, yayin da ‘yan kasar ke nuna rashin jin dadinsu.

“Mun dauki wannan doka a matsayin wani yunkuri na tauye ‘yancin ‘yan Najeriya, kuma muna alfahari da tsayawa tare da jama’a wajen kara zage damtse wajen yin Allah wadai da wannan kudiri na rashin adalci.

“A cikin hadin kai da al’ummar Najeriya, mun yi tir da wannan doka ta danniya, kuma mun sha alwashin kare ‘yancin da tsarin mulki ya ba ‘yan Najeriya.

“Ba za mu daina komai ba don kare duk abin da ya rage na ‘yancin dimokiradiyya a matsayinmu na ‘yan Najeriya, ciki har da tara ‘yan Najeriya a kan tituna idan ba a janye wannan doka mai tsanani ba.”

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp