fidelitybank

Za mu saka ƙafar wando ɗaya da masu maganin gargajiya – Gwamnatin Legas

Date:

Gwamnatin jihar Legas ta ce, za ta sanya takunkumi kan masu magungunan gargajiyan da ke harkokinsu a jihar.

Hukumomi a jihar sun sanya wa’adin ranar 6 ga watan Fabrairu mai kamawa, cewa idan har masu maganin suka ƙi yin rijistar wuraren sana’oinsu da hukumar kula da magungunan gargajiya ta jihar, za su fuskanci takunkumi.

Hakan dai wani mataki ne na kawar da masu magungunan gargajiya na bogi a jihar, a cewar jami’ai.

Magatakardar hukumar kula da magungunan gargajiya ta jihar, Babatunde Aderemi, ya ce yin rajistar zai taimaka wajen tantance masu gaunguna na gaskiya da kuma na jabu.

Haka kuma ya kƙara da cewa duk wasu masu magungunan gargajiyan da dangoginsu da suka kasa sabunta lasisinsu zuwa wannan lokaci, za a cire sunayensu a rajistar.

A cewarsa za a yi hakan ne kamar yadda dokar harkokin lafiya ta jihar ta tanada.

Wasu masu magungunan gargajiya da ke jihar sun yi maraba da matakin, inda suka bayyana buƙatar a yi tantancewar ba tare da wata manufa ba.

Dubban ƴan Najeriya ne ke amfani da magungunan gargajiya saboda dalilan da suka hada da talauci da ƙarancin ƙananan asibitoci a kusa, lamarin da ke jefa rayukansu cikin haɗari.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp