fidelitybank

Za mu rufe Jami’o’in Najeriya – ASUU

Date:

Ƙungiyar malaman jami’o’in Najeriya ASUU ta yi kira ga gwamnatin ƙasar da ta cika yarjejeniyar da suka shiga a shekarar 2009 ko ta tsunduma yajin aiki.

Shugaban ASUU, Chris Piwuna ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a ranar Juma’a a Abuja.

Ya nanata buƙatar da ke akwai na gwamnatin ta cika yarjejeniyar da alƙawuran da ta ɗauka domin magance matsalolin da jami’o’in ƙasar ke fuskanta.

Piwuna ya ce har yanzu akwai wasu muhimman batutuwa guda tara da ba a daddale su ba a yarjejeniyar da suka shiga.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito shi yana cewa daga cikin abubuwan da suka rage akwai albashin malaman da ba a biya ba lokacin da suke yajin aiki na shekarar 2022 da wasu alawus ɗinsu da ake riƙe saboda IPPIS da sauransu.

Ya ce duk da alƙawarin da gwamnati ta yi na zuba naira biliyan 150 domin gudanar da jami’o’in ƙasar da inganta alawus na malaman, har yanzu ba su gani a ƙasa ba.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp