Ƙungiyar malaman jami’o’in Najeriya ASUU ta yi kira ga gwamnatin ƙasar da ta cika yarjejeniyar da suka shiga a shekarar 2009 ko ta tsunduma yajin aiki.
Shugaban ASUU, Chris Piwuna ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a ranar Juma’a a Abuja.
Ya nanata buƙatar da ke akwai na gwamnatin ta cika yarjejeniyar da alƙawuran da ta ɗauka domin magance matsalolin da jami’o’in ƙasar ke fuskanta.
Piwuna ya ce har yanzu akwai wasu muhimman batutuwa guda tara da ba a daddale su ba a yarjejeniyar da suka shiga.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito shi yana cewa daga cikin abubuwan da suka rage akwai albashin malaman da ba a biya ba lokacin da suke yajin aiki na shekarar 2022 da wasu alawus ɗinsu da ake riƙe saboda IPPIS da sauransu.
Ya ce duk da alƙawarin da gwamnati ta yi na zuba naira biliyan 150 domin gudanar da jami’o’in ƙasar da inganta alawus na malaman, har yanzu ba su gani a ƙasa ba.