fidelitybank

Za mu rufe gidajen mai a Kano da suka kaurace farashin da aka tsayar – IPMAN

Date:

Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Najeriya IPMAN, a ranar Juma’a ta yi barazanar rufe gidajen man da ke sayar da fiye da farashin da aka amince.

Sanarwar mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar IPMAN, Alhaji Bashir Dan Malam wanda aka rabawa manema labarai a Kano ta kuma sha alwashin hukunta duk wani dan kasuwa da ya sayar da kayan sama da farashin famfo da aka amince da shi.

Alhaji Bashir Dan Malam ya bayyana bukatar masu zaman kansu da ‘yan kasuwa su sayar da kayan a kan farashi mai inganci domin ba sa biyan karin kudi ga hukumar NNPC kafin samun rabon.

Sai dai ya ja kunnen ‘yan kasuwar da su yi taka-tsan-tsan da wasu mutane da ke da dabi’ar amfani da gidajen man da aka yi musu rajista wajen karbar kaso daga Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL) ba bisa ka’ida ba.

Shugaban na IPMAN ya ce shawarar ta zama wajibi ne biyo bayan korafe-korafe da hukumar ta NNPC ta yi na cewa wasu mutanen da ba su da sana’ar sayar da man fetur suna da dabi’ar karbar kason mai daga kamfanin ba bisa ka’ida ba ta hanyar gabatar da sunayen wasu gidajen man da aka yi wa rajista.

Danmalam ya ce an dauki matakin bayar da gargadin ne a wata ganawa da aka yi tsakanin shugabannin hukumar ta NNPC da kuma shugabannin IPMAN.

A cewarsa, kamfanin ya yi barazanar soke lasisin siyan kaso mai tsoka na duk wani dan kasuwa da aka samu ya bar irin wadannan mutane su yi amfani da gidan man da aka yi wa rajista don samun rabo daga bisani su sayar da kayayyakin ga wasu.
Don haka shugaban na IPMAN ya gargadi masu aikata wannan aika-aika da su daina yin hakan domin duk wanda aka kama za a kai rahoto ga jami’an tsaro domin daukar matakin da ya dace.

Ya kuma kara da cewa hukumar gudanarwar NNPC da ta IPMAN ba za su nade hannayensu ba, su bar irin wannan ta’asa ta ci gaba da cutar da masu sayar da man fetur na gaskiya a kasar nan.

Dan-Malam a cikin sanarwar ya yabawa mahukuntan NNPC da ke karkashin jagorancin Mele Kyari bisa tabbatar da wadatar kayayyakin.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp