fidelitybank

Za mu rufe ɓangaen sadarwa da wutar lantarki a daren Laraba idan aka kama Ajaero – NLC

Date:

Ma’aikatan Najeriya a fannin sadarwa da wutar lantarki sun yi barazanar rufe hanyar sadarwa ta kasa, da kuma na’urorin sadarwa a tsakar daren Laraba idan rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kama shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya Joe Ajaero.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar daban-daban a ranar Talata ta manyan sakatarorin kungiyar ma’aikatan wutar lantarki ta kasa da kungiyar ma’aikatan gidan waya da sadarwa ta kasa Dominic Igwebike da Mary Nwosu, bi da bi.

Hakan na zuwa ne bayan da ‘yan sanda a wata wasika a ranar Litinin ta gayyaci Ajaero domin amsa tambayoyi a ranar Talata kan zargin alaka da bayar da kudaden ta’addanci da wasu zarge-zarge.

Kungiyar ta NLC, a wata wasika da ta aike wa ‘yan sanda a ranar Talata ta ki amsa gayyatar saboda ta zo a makare.

Sai dai ya sanya ranar Laraba 29 ga watan Agusta domin girmama gayyatar.

A halin da ake ciki, dangane da ci gaban, NUEE, NUPTE da sauran kungiyoyin kwadago sun sha alwashin yin watsi da kayan aikin idan aka kama Ajaero.

A cewar sanarwar ga mambobin kungiyar, NUEE, wanda ya kunshi ma’aikata a Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ce: “Duk wani kama shugaban NLC ko wani Shugaban Kwadago, duk ma’aikatan za su sauke kayan aiki daga karfe 12 na dare 21 ga Agusta 2024”.

Hakazalika, NUPTE, ma’aikata a fannin wasiku da sadarwa a Najeriya sun bi umarnin NUEE.

NLC a ranar Talata bayan wani taro da ta yi ta lashi takobin shiga yajin aikin gama gari idan har aka kama Ajaero.

Ci gaban yana nuna haɗari ga tattalin arzikin Najeriya kamar yadda wutar lantarki da sadarwa sune ɗakin injin.

Ku tuna cewa a ranar 3 ga watan Yuni ne aka rufe National grid sakamakon bacewar da aka samu a Najeriya bayan da ma’aikata suka fara yajin aikin sai baba-ta-gani.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp