Hukumar Tarayyar Turai ta ce, za ta mayar da martani domin kare muradun ƴan kasuwa da ma’aikata da kuma masu amfani da kayyayaki bayan shugaba Trump ya ce zai sanya harajin kashi 25 cikin dari kan ƙarafa da sanholo da ake shigarwa Amurka.
Hukumar ta ce ba ta ga dalilin yin hakan ba, inda ta kira matakin da wanda ya saɓa doka kuma zai samar da akasin abin da ake tunani ga tattalin arziƙi.
Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noel Barrot ya ce za su kare muradun Tarayyar Turai babu ƙaƙƙautawa.
Ma’aikatar harkokin wajen China ta buƙaci yin tattaunawa da kuma yarjejeniya, inda ta ce ba a nasara a yaƙin kasuwanci.
Ta buƙaci Amurka ta daina amfani da tattalin arziƙi da cinikayya a matsayin makami.
Tun da farko China ta mayar da martani ta hanyar sanya harajin ramuwa kan kayyayakin da ake shigowa da su daga Amurka da kuɗinsu ya kai dala biliyan 14.