fidelitybank

Za mu mayar wa Trump martani mai zafi don mu kare kan mu – Tarayyar Turai

Date:

Hukumar Tarayyar Turai ta ce, za ta mayar da martani domin kare muradun ƴan kasuwa da ma’aikata da kuma masu amfani da kayyayaki bayan shugaba Trump ya ce zai sanya harajin kashi 25 cikin dari kan ƙarafa da sanholo da ake shigarwa Amurka.

Hukumar ta ce ba ta ga dalilin yin hakan ba, inda ta kira matakin da wanda ya saɓa doka kuma zai samar da akasin abin da ake tunani ga tattalin arziƙi.

Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noel Barrot ya ce za su kare muradun Tarayyar Turai babu ƙaƙƙautawa.

Ma’aikatar harkokin wajen China ta buƙaci yin tattaunawa da kuma yarjejeniya, inda ta ce ba a nasara a yaƙin kasuwanci.

Ta buƙaci Amurka ta daina amfani da tattalin arziƙi da cinikayya a matsayin makami.

Tun da farko China ta mayar da martani ta hanyar sanya harajin ramuwa kan kayyayakin da ake shigowa da su daga Amurka da kuɗinsu ya kai dala biliyan 14.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp