Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya ce kodayake ba yaƙi ne a gaban ƙasarsa ba, amma za ta mayar da martani ”daidai wa daida” kan hare-haren Isra’ila.
Iran ta yi kiran gaggauta taron kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya domin tattauna batun harin, wanda Isra’ila ta kai a matsayin martanin hare-haren makamai masu linzami da Iran ta kai mata a farkon watan da muke ciki.
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya ce hare-haren na ranar Asabar sun faɗa inda aka buƙace su, wato kan masana’antar ƙera makamai masu linzami na ƙasar