Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar wa Isra’ila martani “mai tsanani” idan har suka ci gaba da kai musu hare-hare.
“Sojojin Iran za su mayar da martani mai zafi idan gwamnatin Isra’ila ta ci gaba da far mana,” in ji Pezeshkian.
An ruwaito cewa ya yi kalaman ne a lokacin da yake tattaunawa ta wayar tarho da Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif.