Ministan harkokin wajen Iran, Hossein Amirabdollahian, ya yi gargaɗin cewa ƙasarsa za ta mayar da mummunan martani cikin gaggawa idan Isra’ila ta yi abin da ya saɓa wa muradunta.
Mista Amirabdollahian ya shaida wa kafar yaɗa labaran NBC ta Amurka kasa da kwana guda bayan wani harin da ake kyautata zaton jiragen yakin Isra’ila ne suka kai Isfahan da ke tsakiyar kasar Iran.
Wakiliyar BBC ta ce takaitaccen harin isra’ila, wanda ba ta ɗauki alhaki ba a hukumance, ya ba Iran damar sassautawa kafin daukar mataki.
Martanin da Tehran ta yi a ranar Juma’a – wanda ta yi watsi da al’amuran da suka faru a safiyar Juma’a – ya nuna alamun za a iya kwantar da tarzoma tsakanin ɓangarorin biyu masu rikici da juna