fidelitybank

Za mu ladabtar da Jami’an mu da aka gansu suna taimakawa ‘yan siyasa a Kano – ‘Yansanda

Date:

Rundunar ƴan sanda ta jihar Kano ta ce, ta ɗauki matakin ladabtarwa a kan jami’anta biyar da aka gani a faifan bidiyo suna taimaka wa wani ɗan siyasa wajen shirya jama’a domin karɓar kuɗi a gidan gwamnatin jihar.
Sanarwar da mai magana da yawun rundunar ‘yansandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar a madadin kwamishinan ƴan sandan jihar Kano a ranar Talata, 19 ga Agusta, 2025.
Sanarwar ta bayyana cewa bincike ya gano lamarin ya faru ne bayan wani taro a ɗakin taro na Coronation Hall da ke gidan gwamnati na Kano a ranar 10 ga Yuli, 2025, kuma bai da wata alaka da zaɓen cike gurbi da aka gudanar a jihar a ranar 16 ga Agusta, 2025.
Rundunar ta ce jami’an sun aikata rashin kwarewa yayin da aka tura su aikin tsaro, kuma yanzu haka an fara ɗaukar matakan ladabtarwa a kansu domin tabbatar da tsari da kare mutuncin rundunar.
Haka kuma, an jaddada cewa rundunar ƴan sanda za ta ci gaba da jajircewa wajen bin ƙa’idoji da kiyaye amana da ɗabi’a domin samun amincewar jama’a.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp