fidelitybank

Za mu kuɓutar da ɗan Majalisar Anambra da aka sace a matarsa – Ƴansanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta gano motar dan majalisar dokokin jihar, Honourable Justice Azuka, wanda ke wakiltar mazabar Onitsha North, bayan an yi garkuwa da shi ranar Talata, 24 ga Disamba, 2024, a garin Onitsha.

Kamar yadda DailyPost ta ruwaito, wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba sun yi garkuwa da Azuka a yayin da yake dawowa gida don bikin Kirsimeti.

A wata sanarwa da mai magana da yawun ‘yan sandan jihar, Tochukwu Ikenga, ya fitar, ya bayyana cewa motar dan majalisar da aka yi garkuwa da shi an gano ta ne a lokacin aikin ceto da jami’an sashen Inland Town Division suka gudanar.

A cewarsa: “Bayan wani aiki mai zurfi da ke ci gaba, jami’an rundunar daga sashen Inland Town Division sun gano motar Honourable Justice Azuka, wanda aka yi garkuwa da shi ranar 24 ga Disamba, 2024, misalin karfe 9:20 na dare a kan titin Ugwunapampa, Onitsha.”

Ikenga ya bayyana cewa an gano motar ne a kan titin Upper Iweka ta hannun tawagar ceto. Sai dai har yanzu ba a gano inda Azuka yake ba, amma rundunar tana kara kaimi don ganin an kubutar da shi cikin koshin lafiya.

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Nnaghe Obono Itam, ya umurci jami’an da su ninka kokarinsu don tabbatar da cewa an kubutar da dan majalisar cikin gaggawa.

“Mun dauki wannan lamari da matukar muhimmanci, kuma muna kira ga al’ummar gari da su taimaka wa ‘yan sanda da duk wani bayani da zai taimaka wajen ceton Honourable Justice Azuka,” in ji Ikenga.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp