fidelitybank

Za mu koma fagen daga idan Hamas ba ta saki ‘yan kasar mu ba – Isra’ila

Date:

Isra’ila ta ce za ta koma yaƙi tare da fatali da yarjejeniyar tsagaita wuta, matsawar Hamas ba ta saki Isra’ilawan da ke take garkuwa da su ba a ranar Asabar.

Firaministan Isra’ila Benjami Netanyahu bai fayyace ko yana nufin duka mutanen da Hamas din ke garkuwa da su, ko kuma ukun da aka tsara saki a ranar ƙarƙashin yarjejeniyar.

Netanyahu ya umarci dakarun ƙasarsu su taro a ciki da kewayen Gaza, yayin da Hamas ke cewa Isra’ila ce ”ta janyo duk abin da ya faru na jinkirin da aka samu”.

Ƙungiyar ta ce ta jinkirta sakin mutanen da aka tsara za ta saki a ƙarshen makon da muke ciki, bayan da ta zargi Isra’ila da saɓa wa sharuɗan yarjejeniyar, sai dai ta ce har yanzu tana son ci gaba da aiki da yarjejeniyar.

An fahimci cewa ƙasashen Larabawa na matsa wa ƙungiyar lamba kan komawa aiki da yarjejeniyar.

Tun da farko shugaban Amurka, Donald Trump ya yi gargaɗin cewa idan ba a saki Isra’ilawan da Hamas ke garkuwa da su a Gaza ba ”za a yi duk bala’in da za a yi”, matakin da Netanyahu ya yi maraba da shi a ranar Talata.

Kawo yanzu Falasɗinawa da suka koma Gaza byan fara aiki da yarjejeniyar, na cikin fargaba da tashin hankali.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp