Isra’ila ta ce za ta koma yaƙi tare da fatali da yarjejeniyar tsagaita wuta, matsawar Hamas ba ta saki Isra’ilawan da ke take garkuwa da su ba a ranar Asabar.
Firaministan Isra’ila Benjami Netanyahu bai fayyace ko yana nufin duka mutanen da Hamas din ke garkuwa da su, ko kuma ukun da aka tsara saki a ranar ƙarƙashin yarjejeniyar.
Netanyahu ya umarci dakarun ƙasarsu su taro a ciki da kewayen Gaza, yayin da Hamas ke cewa Isra’ila ce ”ta janyo duk abin da ya faru na jinkirin da aka samu”.
Ƙungiyar ta ce ta jinkirta sakin mutanen da aka tsara za ta saki a ƙarshen makon da muke ciki, bayan da ta zargi Isra’ila da saɓa wa sharuɗan yarjejeniyar, sai dai ta ce har yanzu tana son ci gaba da aiki da yarjejeniyar.
An fahimci cewa ƙasashen Larabawa na matsa wa ƙungiyar lamba kan komawa aiki da yarjejeniyar.
Tun da farko shugaban Amurka, Donald Trump ya yi gargaɗin cewa idan ba a saki Isra’ilawan da Hamas ke garkuwa da su a Gaza ba ”za a yi duk bala’in da za a yi”, matakin da Netanyahu ya yi maraba da shi a ranar Talata.
Kawo yanzu Falasɗinawa da suka koma Gaza byan fara aiki da yarjejeniyar, na cikin fargaba da tashin hankali.