Gidauniyar Sheikh Ɗahiru Bauchi ta yi barazanar ko dai tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya nemi afuwar ɗaliban shehin malamin kan rashin adalcin da ta ce ya musu, ko kuma su maka shi a kotu.
Wannan na ƙunshe a wata takarda da gidauniyar ta fitar, wadda Sayyadi Aliyu Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya sanya wa hannu, inda gidauniyar ta ce sun ba El-Rufai nan da zuwa ƙarshen watan Ramadan.
Sayyadi ya ce dole ne El-Rufai ya fito ya bayyana cewa ya yi laifi, “sannan ya nemi afuwar gidauniyar da ɗalibanta da ma jagoranmu.”
Takardar ta zargi El-Rufai ba ” jami’an tsaro umarni su samame a makarantun tsangayarmu. Sun je har gidan malaminmu, Sheikh Ɗahiru Bauchi suka kwashe ɗaliban makarantarmu masu karatun Qur’ani. Kuma har yanzu akwai ɗaliban da ba mu san inda suke ba.”
Sayyadi ya ƙara da cewa, “an yi samamen ne da gangan domin a tozarta Sheikh Ɗahiru Bauchi da ɓata aikin da ya ɗauki tsawon rayuwarsa yana yi na ilimantar da al’umma da tabbatar da zaman lafiya.”
Sayyadi ya ce idan har zuwa ƙarshen Ramadan El-Rufai bai fito ya bayar da haƙuri ba, “za mu kai ƙararsa wajen shugaban ƙasa da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan’adam da ma kotu domin a ƙwato mana haƙƙinmu.
“Idan kuma duka ba su yi mana adalci ba, za mu kai ƙararsa wajen Allah ta hanyar addu’o’i.”