fidelitybank

Za mu jagoranci kudirin janye karin wutar lantarki – Ndume

Date:

Babban mai tsawatarwar Majalisar Dattijai, Sanata Muhammad Ali Ndume, ya ce, ba wannan ne lokacin da ya dace a yi ƙarin kuɗin wutar lantarki ba ga ‘yan ƙasa.

Cikin wata tattaunawa da ya yi da BBC Sanata Ndume ya ce wutar da babu ita ta yaya za a yi ƙarin kuɗi a kanta, ya shawarci gwamnati da ta fara samar da ita gabanin yin ƙarin kudinta.

“Babbar maganar ita ce kamfanonin da aka raba musu tashoshin bayar da wutar nan ba su biya kudaden ba ma tukunna har yau. Na biyu babu wutar, tun da aka ba su ba su habbaka yayyukansu ba.

“Gwamnati ta cefananr da wutar da zimmar ko za ta habbaka, amma kullum ƙara taɓarɓarewa take yi,” in ji Sanatan.

Ya ce da zarar majalisarsu ta koma hutu a ranar 16 ga watan Afrilu, shi da wasu abokan aikinsa za su jagoranci gabatar da ƙuduri kan janye wannan ƙarin.

Za kuma su bayyana cewa ya kamata duk abin da za a yi da ya shafi rayuwar talakawa ya ji ra’ayoyinsu gabanin aiwatar da shi, za kuma a iya cimma haka ne ta sauraren ra’ayinsu ‘yan majalisa a matsayin wakilan al’umma.

“Kamata ya yi idan za a ƙara kuɗin wuta a samar da ita, a ƙara albashin ma’aikata sannan a tabbatar da hauhawar farashin kayayyaki ya yi ƙasa”.

Ya kuma ce abin kunya ne raba wutar lantarki mataki daban-daban, akwai ta masu kuɗi akwai ta talakawa.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp