Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC), ta musanta rahotannin da ke cewa tana daukar ma’aikata.
Hukumar ta musanta hakan ne a wasu jerin sakonnin da ta wallafa a shafinta na Twitter ranar Lahadi.
Hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa ta ce, wata sanarwa da ta gayyaci wadanda ba su ji ba, da su gabatar da aikace-aikacen ta hanyar wata hanyar da EFCC ta dauka na daukar ma’aikata 2023/2024 mai kwanan wata 7 ga Afrilu 2023 karya ce.
“Hukumar na son sanar da jama’a cewa, a halin yanzu ba ta daukar ma’aikata. Duk wani bayani akasin haka da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani karya ne kuma aikin miyagu ne da nufin damfarar masu neman aiki marasa galihu.
“Hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ci gaba da yin amfani da cikakken fushin dokar don gurfanar da masu laifin,” in ji ta.