fidelitybank

Za mu hukunta jami’an mu da suka taka wani a mota – Sufeton ‘Yan Sanda

Date:

Muƙaddashin babban Sifeton ‘yan sanda na kasa Olukayode Adeolu Egbetokun, ya yi Allah wadai da wasu jami’an rundunar ‘yan sanda da suka tuƙa mota suka bi ta kan wani mutum a wani lamari da ya faru ranar Alhamis a jihar Edo da ke kudu maso kudancin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na Twitter, ta ce mukaddashin Babban Sifeton ‘yan sandan ya bayar da umarni ga jami’an ‘yan sandan – waɗanda yanzu haka ke tsare a Edo – da su hallara a shalkwatar hukumar da ke Abuja ranar Litinin domin ɗaukar mataki a kansu.

Cikin wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta an ga yadda jami’an ‘yan sandan suka tuka wata mota tare da bin ta kan wani mutum da ake tunani direban motar ne, da ya kwanta a gaban motar, lamarin da ya jefa mutanen da ke wajen cikin firgici.

Sanarwar ‘yan sandan ta yi kira ga al’umma musamman mutanen garin Ekpoma da su kwantar da hankulansu, tare da alƙawarta cewa rundunar ‘yan sandan ba za ta lamunci irin wannan mummunan aika-aika da wasu ɓata-garin jami’anta ke yi ba.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp