Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce, ba za su zuba idanu ba, shugabannin ƙananan Hukumomi da Kansilolin su, su ce kuɗaɗen al’umma ba, ba tare da sun ɗauki matakin ladabtar da su ba.
Gwamnan ya bayyana hakan ne bayan jawabinsa na yau da ya yi, yayin kaɗa kuri’ar sa a mazaɓarsa ta Gwale.
Ya kuma ce “Akwai matakai da za mu bi, wajen hukunta duk wani da mu ka samu da rubda ciki da duniyoyin al’umma, saboda haka ku fito ku yi wa al’ummar ku aiki tuƙuru”. In ji Abba.