fidelitybank

Za mu haɗa hannu da Saudiyya don inganta makarantun allo – Gwamnatin Jigawa

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa za ta haɗa hannu da gidauniyar ‘Alfurqan Qur’anic’ ta ƙasar Saudiyya don inganta makarantun tsangaya da ke faɗin jihar.

Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran gwamnan, Hamisu Mohammed Gumel ya fitar, ya ce an cimma hakan ne bayan wata ziyara da shugaban gidauniyar, Sheikh Abdalla Ibn Nasir Al-Utaibiy, ya kai wa gwamnan jihar, Mallam Umar Namadi ranar Juma’a a gidan gwamnatin jihar da ke Dutse.

Sheikh Al-Utaibiy, ya ce manufar haɗin gwiwar shi ne zamanantar da hanyoyin karatun allo domin sauƙaƙa hanyoyin koyon karatun da kuma haddar Al-qur’anin mai tsarki.

Ya ƙara da cewa gidauniyarsa ta ƙware wajen amfani da hanyoyin zamani na koyon karatun alqur’ani da kuma sauƙaƙa koyar da shi ga masu lalurar ji (kurame) da ƙananan yara.

Jihar Jigawa na daga cikin jihohin ƙasar da ake tura ƙananan yara makarantun Allo na gargajiya da ake kira ‘almajirci’ domin samun ilimin alqur’ani.

Wasu iyayen kan tura yaran zuwa makarantun tsangayar ba tare da tanadar musu abincin da za su ci ba, inda a wasu lokutan yaran kan ƙare a bin gidajen mutane da kasuwanni da kan tituna suna barar abincin da za su ci

Wani abu da masana da gwamnatoci ke ganin rashin dacewarsa, suna masu fargabar hakan ka iya jefa rayuwar ƙananan yaran cikin hatsari.

A nasa ɓangare gwamnan jihar jigawa, Mallam Umar Namadi ya ce gwamnatinsa na gudanar da wasu tsare-tsare don inganta makarantun tsangayar da ke faɗin jihar, ta hanyar haɗa wa yaran da ilimin boko da koya musu sana’o’in da za su dogara da kansu.

Ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta gina manyan makarantun tsangaya na zamani a shiyoyin jihar uku, da nufin samar wa jihar malaman qur’ani masu ƙwarewar sana’o’in hannu, sannan suke da wayewa ta fannin ilimin boko.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp