Ƙungiyoyin ma’aikatan jiragen sama sun yi barazanar rufe filayen tashi da saukar jiragen sama a Najeriya daga ranar 31 ga Maris, 2025.
Ma’aikatan sun ce za su ɗauki matakin ne idan gwamnati ba ta kori jami’in kwastam da suke zargi da hannu wajen cin zarafin daraktan tsaro a hukumar kula da filayen jiragen sama ta ƙasar ba.
Haɗakar ƙungiyoyin sun fitar da sanarwar hadin guiwa tare da bayyana rashin gamsuwarsu kan abin da jami’in hana fasakwaurin ya aikata.
Ƙungiyoyin sun koka kan yawaitar cin zarafin da ma’aikatan hukumar kula da filayen jiragen saman ƙasar ke ci gaba da fuskanta.
Hukumar kwastam ta ƙasar ta bayyana abin da ya faru a filin jiragen sama na Murtala Muhammed da ke Legas a matsayin rashin fahimta da ta janyo rashin jituwa tsakaninsa da daraktan.
Kakakin hukumar na ƙasa, Abdullahi Mai Wada Aliyu ya bayyana ƙudirin hukumar na jaddada haɗin guiwa tsakanin hukumomi.
Wanda hakan ya haɗa da mutunta juna da inganta yanayin aiki tare.