fidelitybank

Za mu hada kan kungiyar ECOWAS – Barau Jibrin

Date:

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin ya ce suna da kuduri na ganin sun haɗa kan ƙungiyar Ecowas.

Barau ya bayyana haka ne yayin tattaunawa da BBC, inda ya ce ya zama wajibi Ecowas ta haɗa kai domin samun ci gaba da ya kamata.

“Kafin zuwan Turawa, ƙasashen Afrika ta Yamma ko Ecowas sun kasance ƙasa ɗaya. Ana yin Hausa a kowane yanki ka je kama daga Nijar, Mali, Ghana da sauransu haka ma ga duka sauran yaruka”.

“Bayan zuwan Turawa ne suka raba kawunanmu, kuma ya kamata mu haɗa kai yanzu,” in ji Barau.

Ya ce idan ana haɗe za a fi samun ci gaba, walwala da kuma jin daɗi na al’umma.

Mataimakin shugaban majalisar ta dattawa ya ce za su yi duk abin da za su iya wajen hada kan mambobin kungiyar ta Ecowas.

Ya kuma ce suna da kudurin ganin an samar da kudi bai-daya na kasashen.

Barau ya ce suna da kudurin kawo tsarin da zai kawo hadin kai ta hanyar tattalin arziki, tsaro da kuma ci gaban yankin.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp