fidelitybank

Za mu haɗa hannu da Saudiyya don inganta makarantun allo – Gwamnatin Jigawa

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa za ta haɗa hannu da gidauniyar ‘Alfurqan Qur’anic’ ta ƙasar Saudiyya don inganta makarantun tsangaya da ke faɗin jihar.

Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran gwamnan, Hamisu Mohammed Gumel ya fitar, ya ce an cimma hakan ne bayan wata ziyara da shugaban gidauniyar, Sheikh Abdalla Ibn Nasir Al-Utaibiy, ya kai wa gwamnan jihar, Mallam Umar Namadi ranar Juma’a a gidan gwamnatin jihar da ke Dutse.

Sheikh Al-Utaibiy, ya ce manufar haɗin gwiwar shi ne zamanantar da hanyoyin karatun allo domin sauƙaƙa hanyoyin koyon karatun da kuma haddar Al-qur’anin mai tsarki.

Ya ƙara da cewa gidauniyarsa ta ƙware wajen amfani da hanyoyin zamani na koyon karatun alqur’ani da kuma sauƙaƙa koyar da shi ga masu lalurar ji (kurame) da ƙananan yara.

Jihar Jigawa na daga cikin jihohin ƙasar da ake tura ƙananan yara makarantun Allo na gargajiya da ake kira ‘almajirci’ domin samun ilimin alqur’ani.

Wasu iyayen kan tura yaran zuwa makarantun tsangayar ba tare da tanadar musu abincin da za su ci ba, inda a wasu lokutan yaran kan ƙare a bin gidajen mutane da kasuwanni da kan tituna suna barar abincin da za su ci

Wani abu da masana da gwamnatoci ke ganin rashin dacewarsa, suna masu fargabar hakan ka iya jefa rayuwar ƙananan yaran cikin hatsari.

A nasa ɓangare gwamnan jihar jigawa, Mallam Umar Namadi ya ce gwamnatinsa na gudanar da wasu tsare-tsare don inganta makarantun tsangayar da ke faɗin jihar, ta hanyar haɗa wa yaran da ilimin boko da koya musu sana’o’in da za su dogara da kansu.

Ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta gina manyan makarantun tsangaya na zamani a shiyoyin jihar uku, da nufin samar wa jihar malaman qur’ani masu ƙwarewar sana’o’in hannu, sannan suke da wayewa ta fannin ilimin boko.

latest news in lokoja, kogi state

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp