fidelitybank

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Date:

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa ta fara yunƙurin gyara tsarin birnin jihar domin kiyaye jihar daga ambaliya.

Zulum ya bayyana haka ne jim kaɗan bayan ziyarar gani da ido da ya yi wajen gyara da ake yi a dam ɗin Alau, inda ya ce har yanzu akwai wasu da suke gini a magudanan ruwa da kuma masu zuba shara suna toshe magudunan ruwa.

“Za mu duba tare da gyara tsarin birnin Maiduguri domin mu tabbatar dukkan magudanan ruwanmu a buɗe suke kuma suna aiki,” in ji shi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Ya yi gargaɗin cewa duk wani gini da aka yi a magudunan ruwa za a rushe su.

Ya ce za su ɗauki matakin rusau ɗin ne domin kare sake aukuwar irin ambaliya da ta auku a ranar 10 ga watan Satumban 2024 a Jere da ke Maiduguri.

A game da fargabar da ake yi a Maiduguri na sake aukuwar ambaliyar, Zulum ya buƙaci ƴan jihar su kwantar da hankalinsu, inda ya ce akwai babbar ma’adana ta dam ɗin Alau ɗin, da ya ce za ta janye ruwan idan ya cika.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...
X whatsapp