fidelitybank

Za mu gina wa ƴan Najeriya gidaje dubu biyar-biyar a kowace shiyya – Gwamnatin Tarayya

Date:

Gwannatin Tarayya ta ce, tana shirin gina gidaje dubu biyar-biyar a dukkan shiyyoyi shida na kasar, don bunkasa samar da gidaje.

Ƙaramin ministan gidaje da raya karkara na Najeriya Alhaji Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo ne ya bayyana haka yayin wata tattaunawa da BBC dangane da bikin ranar inganta wuraren zama da gidaje na wannan shekara.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta ɓullo da wannan rana ne da manufofi daban-daban ciki har da rage yawan tururuwar al’umma zuwa birane.

Gwamnatin Najeriya ta ce dama akwai wannan tsari na gina gidaje a ƙasar, amma kasancewar wannan ma’aikatar a baya tana ƙarƙashin ma’aikatar ayyuka da makamashi. Amma yanzu an cire ta daga nan kuma za ta fara aiki gadan-gadan.

“Muna da shirin gina gidaje dubu dai-dai a kowacce jiha. Muna jiran Shugaban ƙasa ya sahhale mana ne sannan mu ƙaddamar da aikin.

“Akwai tsarin bai wa waɗanda ba su da gata kyauta, wasu kuma a ba su cikin farashi mai sauki,” in ji T Gwarzo.

Ministan ya ce sun kammala tsare-tsare da zane-zanensu, iyakaci su ƙaddamar da wannan aiki nan ba da jimawa ba.

Ya ƙara da cewa aikin na da fuska biyu, na farko akwai wanda ake kira ‘Mega City’ wato manyan birane, shi ne za a gina gidaje dubu biyar a kowacce shiyya ta Najeriya.

Amma ya ce faruwar aikin ta ta allaƙa ne da gabatar da kasafin kuɗi wanda za a yi nan ba da jimawa ba.

Ka shi na biyu shi ne, na raya karkara, wanda za a je ƙananan hukumomi a yi hanyoyi a fitar da titi da kasuwanni ta yadda za su zama kai ɗaya da birane, kamar yadda ministan ya bayyana

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp