fidelitybank

Za mu gina sabon shataletalen gidan gwamnatin – Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta ce, za ta gina sabon shataletale a gaban gidan gwamnatin jihar.

Bayan da ta rushe tsohon shataletalen sakamakon dalilai na tsaro kamar yadda gwamnatin ta bayyana.

A cikin wata sanarwa da Sakataren yaɗa labaran gwamna Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce gwamnatin jihar ta tuntuɓi injiniyoyi a fannin gine-gine domin yin nazari game da ginin shataletalen kafin ta rusa shi.

A cewar sanarwar injiniyoyin sun ce ginin ba shi da inganci kuma zai iya faɗuwa tsakanin shekarar 2023 zuwa 2024.

Saboda a cewarsu an gina shi da kayyaki marasa inganci, a maimakon amfani da tsantsar siminti da kyakkyawan kankare.

Haka kuma sanarwar ta ci gaba da cewa masanan sun bai wa gwamnati shawarar cewa ginin ya yi tsawo a gina shi a gaban gidan gwamnatin jihar, saboda ya tokare babbar kofar gidan.

Sanarawar ta ƙara da cewa ginin na haifar wa direbobi matsaloli saboda yadda yake rufe musu ganin sauran hanyoyin da ke da mahaɗa a shataletalen.

Kan hakan ne gwamnatin jihar ta ce ya zama wajibi ta rushe ginin, domin sake fasalin ginin ta yadda za ta rage tsayinsa ta yadda za a riƙa hango babbar ƙofar shiga gidan gwamnatin tare da kare masu ababen hawa.

Rahotonni sun ce an wayi gari da ganin motocin rusau a kan ginin shataletalen da ke gaban gidan gwamnatin jihar.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp