fidelitybank

Za mu gina madatsaun ruwa biyar domin tare ruwan dam ɗin Lagdo – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Tarayya ta bakin Hukumar Ruwa ta Najeriya wato Nigeria Hydrological Services Agency (NIHSA) ta ce za ta gina wasu madatsun ruwa biyar domin kare ambaliyar da ke faruwa a sanadiyar ruwan da ke mamal daga dam ɗin Lagbo na Kamaru.

Darakta-Janar na NIHSA, Umar Mohammed ne ya bayyana hakan a zantawarsa ta talabijin na Channels a ranar Alhamis.

Hukumar ta gargaɗi ƴan Najeriya da suke zaune a wuraren da ake ambaliya su canja mazauni saboda sako ruwan da aka yi daga Kamaru.

Jihohin da ake fargabar dam ɗin na Kamaru zai jawo ambaliya sun haɗa da Adamawa da Taraba da Benue da Nasarawa da Kogi da Edo da Delta da Anambra da Bayelsa da Kuros Riba da Rivers.

Mohammed, wanda daraktan aikace-aikace na hukumar Femi Bejide ya wakilta, ya ce hukumar ta miƙa wa Fadar Shugaban Ƙasa rahoto, inda a ciki ta bayyana hanyoyin da za a kiyaye aukuwar ambaliyar, ciki har da sauya wuraren da wasu dam suke.

“Sannan mun miƙa buƙatar gina wasu dam guda biyar domin tare ruwan dam ɗin Lagdo,” in ji shi.

“Amma dole za a canja inda wasu dam suke, sannan a faɗaɗa gaɓar tekunan Neja da Benuwe.”

Sako ruwan dam ɗin Lagdo ya zo ne kwanaki kaɗan bayan dam ɗin Alau a Maiduguri ya yi ambaliya, inda aƙalla mutum 30 suka mutu, sannan ya raba dubbai da muhallansu.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp