Najeriya za ta fara kwaso ƴan ƙasarta da suka tsallaka makwabtan Ukraine domin gujewa yaƙi, kamar yadda ministan harakokin waje ya bayyana.
Ministan ya ce, a ranar Laraba jiragen za a fara kwaso ƴan Najeriya da suke son dawowa.
Ya kuma ce, kimanin ƴan Najeriya 5,600 har yanzu ke Ukraine, yawancinsu ɗalibai kuma ana ƙoƙarin ganin yadda za su tsallaka ƙasashe makwabta Romania da Poland da Slovakia da Hungary.
Ukraine ta rufe filayen jiragen samanta bayan mamayar Rasha.
Daruruwan ƴan Najeriya tuni suka fice daga Ukraine ta jiragen ƙasa da motocin bas.
Amma ƴan Afirka sun koka kan yadda ake nuna masu wariya a iyakokin Ukraine inda ake hana masu shiga jiragen kasa da motoci da ke ɗaukar ƴan ƙasashen waje da ke ƙauracewa rikicin.