fidelitybank

Za mu fara hako fetur a yankin Arewa – NNPCL

Date:

Babban Jami’in Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL), Bayo Ojulari, ya bayyana shirin ci gaba da ayyukan hakar danyen mai a garin Kolmani da ke tsakanin jihohin Gombe da Bauchi.

Ojulari ya bayyana hakan ne a wata hira da yayi da BBC Hausa.

A cewarsa, kamfanin ya shirya tsaf don komawa gidajen mai na Kolmani, wanda ya haifar da kyakkyawan fata a tsakanin al’ummar Arewa lokacin da aka fara hakar mai.

“NNPCL a shirye yake ya dawo da aikin hakar mai a Kolmani, mun kammala tantancewa kuma muna shirin ci gaba,” in ji Ojulari.

Ya kuma jaddada cewa aikin ba wai don bunkasa yawan man da ake hakowa a kasa ba ne, har ma da kara habaka tattalin arzikin yankin.

ā€œWannan yunkurin zai kawo ci gaba a Arewa, zai jawo sabbin masana’antu, da kuma farfado da wadanda ake da su,ā€ in ji shi.

Ojulari ya kara da cewa, tare da ayyukan Kolmani, kamfanin na NNPC yana kuma ci gaba da gudanar da ayyukan samar da iskar gas, musamman bututun iskar gas daga Ajaokuta – Kano (AKK).

Ya ce bututun zai taimaka wajen samar da wutar lantarki da kuma rage tsadar sufuri a fadin arewacin Najeriya.

“Ni dan Arewa ne daga Kwara, na girma a Kaduna kuma na fara koyon harshen Yarbanci tun ina shekara 15. Na yi karatu a Zariya,” in ji shi.

ā€œIna son jama’ar Arewa su ba ni goyon baya a wannan aiki domin a hada kai mu kawo ci gaba a yankin da Nijeriya baki daya.

Da yake magana kan rashin jituwar da ake zargin Dangote da kamfanin NNPC, ya yabawa Aliko Dangote tare da ba da tabbacin cewa kamfanin na NNPC zai yi aiki kafada da kafada da shi don ganin ā€˜yan Najeriya sun samu saukin man fetur.

Ya jaddada cewa jama’a ba za su kara jin wani rikici tsakanin kamfanin NNPC da na Dangote.

A watan Nuwambar 2022 ne shugaba Buhari ya kaddamar da aikin hako mai na Kolmani a matsayin wani mataki mai cike da tarihi na karkatar da man da Najeriya ke hakowa fiye da yankin Neja Delta.

Koyaya, ayyukan sun tsaya cik saboda kalubalen fasaha da kayan aiki.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ʙai ta Majalisar ʊinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

ʘungiyoyin kare haʙʙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

ʘungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ʓansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ʙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban ʘsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...
X whatsapp