fidelitybank

Za mu fara hako fetur a yankin Arewa – NNPCL

Date:

Babban Jami’in Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL), Bayo Ojulari, ya bayyana shirin ci gaba da ayyukan hakar danyen mai a garin Kolmani da ke tsakanin jihohin Gombe da Bauchi.

Ojulari ya bayyana hakan ne a wata hira da yayi da BBC Hausa.

A cewarsa, kamfanin ya shirya tsaf don komawa gidajen mai na Kolmani, wanda ya haifar da kyakkyawan fata a tsakanin al’ummar Arewa lokacin da aka fara hakar mai.

“NNPCL a shirye yake ya dawo da aikin hakar mai a Kolmani, mun kammala tantancewa kuma muna shirin ci gaba,” in ji Ojulari.

Ya kuma jaddada cewa aikin ba wai don bunkasa yawan man da ake hakowa a kasa ba ne, har ma da kara habaka tattalin arzikin yankin.

ā€œWannan yunkurin zai kawo ci gaba a Arewa, zai jawo sabbin masana’antu, da kuma farfado da wadanda ake da su,ā€ in ji shi.

Ojulari ya kara da cewa, tare da ayyukan Kolmani, kamfanin na NNPC yana kuma ci gaba da gudanar da ayyukan samar da iskar gas, musamman bututun iskar gas daga Ajaokuta – Kano (AKK).

Ya ce bututun zai taimaka wajen samar da wutar lantarki da kuma rage tsadar sufuri a fadin arewacin Najeriya.

“Ni dan Arewa ne daga Kwara, na girma a Kaduna kuma na fara koyon harshen Yarbanci tun ina shekara 15. Na yi karatu a Zariya,” in ji shi.

ā€œIna son jama’ar Arewa su ba ni goyon baya a wannan aiki domin a hada kai mu kawo ci gaba a yankin da Nijeriya baki daya.

Da yake magana kan rashin jituwar da ake zargin Dangote da kamfanin NNPC, ya yabawa Aliko Dangote tare da ba da tabbacin cewa kamfanin na NNPC zai yi aiki kafada da kafada da shi don ganin ā€˜yan Najeriya sun samu saukin man fetur.

Ya jaddada cewa jama’a ba za su kara jin wani rikici tsakanin kamfanin NNPC da na Dangote.

A watan Nuwambar 2022 ne shugaba Buhari ya kaddamar da aikin hako mai na Kolmani a matsayin wani mataki mai cike da tarihi na karkatar da man da Najeriya ke hakowa fiye da yankin Neja Delta.

Koyaya, ayyukan sun tsaya cik saboda kalubalen fasaha da kayan aiki.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ʙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar ʊangote wajen haʙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ā€˜Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Ę“an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp