Babban Jamiāin Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL), Bayo Ojulari, ya bayyana shirin ci gaba da ayyukan hakar danyen mai a garin Kolmani da ke tsakanin jihohin Gombe da Bauchi.
Ojulari ya bayyana hakan ne a wata hira da yayi da BBC Hausa.
A cewarsa, kamfanin ya shirya tsaf don komawa gidajen mai na Kolmani, wanda ya haifar da kyakkyawan fata a tsakanin alāummar Arewa lokacin da aka fara hakar mai.
“NNPCL a shirye yake ya dawo da aikin hakar mai a Kolmani, mun kammala tantancewa kuma muna shirin ci gaba,” in ji Ojulari.
Ya kuma jaddada cewa aikin ba wai don bunkasa yawan man da ake hakowa a kasa ba ne, har ma da kara habaka tattalin arzikin yankin.
āWannan yunkurin zai kawo ci gaba a Arewa, zai jawo sabbin masanaāantu, da kuma farfado da wadanda ake da su,ā in ji shi.
Ojulari ya kara da cewa, tare da ayyukan Kolmani, kamfanin na NNPC yana kuma ci gaba da gudanar da ayyukan samar da iskar gas, musamman bututun iskar gas daga Ajaokuta ā Kano (AKK).
Ya ce bututun zai taimaka wajen samar da wutar lantarki da kuma rage tsadar sufuri a fadin arewacin Najeriya.
“Ni dan Arewa ne daga Kwara, na girma a Kaduna kuma na fara koyon harshen Yarbanci tun ina shekara 15. Na yi karatu a Zariya,” in ji shi.
āIna son jamaāar Arewa su ba ni goyon baya a wannan aiki domin a hada kai mu kawo ci gaba a yankin da Nijeriya baki daya.
Da yake magana kan rashin jituwar da ake zargin Dangote da kamfanin NNPC, ya yabawa Aliko Dangote tare da ba da tabbacin cewa kamfanin na NNPC zai yi aiki kafada da kafada da shi don ganin āyan Najeriya sun samu saukin man fetur.
Ya jaddada cewa jamaāa ba za su kara jin wani rikici tsakanin kamfanin NNPC da na Dangote.
A watan Nuwambar 2022 ne shugaba Buhari ya kaddamar da aikin hako mai na Kolmani a matsayin wani mataki mai cike da tarihi na karkatar da man da Najeriya ke hakowa fiye da yankin Neja Delta.
Koyaya, ayyukan sun tsaya cik saboda kalubalen fasaha da kayan aiki.