Ministar harkokin wajen Australia ta bayar da hasken cewa ƙasarta za ta fara ɗaukar yankin Falasɗinu a matsayin ƙasa mai zaman kanta, don ganin yadda za a gaggauta samun zaman lafiya a yankin.
Kuma Hamas ba za ta samu mazauni ba a gwamnatinta in ji Penny Wong.
‘Yan adawa a gwamnatin Australia sun ce ya zuwa yanzu ƙudurin bai kankama ba.
Suna cewa ba yadda za a yi a ɗauki yankin Falasɗinu a matsayin ƙasa sai dai idan an amince a samar da ƙasashe guda biyu tsakaninta da Isra’ila.
Wannan furuci na Wong na zuwa ne bayan da sakataren harkokin wajen Burtaniya David Cameron ya nemi shi ma a samar da ƙasashen biyu a farkon wannan shekara, inda ya ce kamata ya yi Burtaniya ta amince da ƙasar Falasdinu ko da Isra’ila ba ta amince ba.
A kwanan nan gwamnatin Australia na nuna damuwa kan yain da ake da Hamas a Gaza – ciki har da kashe wani jami’in aikin ceto da wasu mutum shida yayin wani harin da Isra’ila ta kai.
A bayanin da ta yi a daren Talata – Wong ta ce samar da ƙasashe biyu shi ne zai zama mafita ga wannan rikici, Isra’ila da Falasdinawa kowa ya zauna a ɓangarensa. In ji BBC.