fidelitybank

Za mu dauki matakin kare Al’kurani – Kungiyar Kasashen Musulmi

Date:

Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta nemi a ɗauki matakin kauce wa sake ƙona Ƙur’ani, ‘yan kwanaki bayan wani ya ƙona kwafin littafin mai tsarki a Sweden.

Ƙungiyar mai mamba 57 ta gana a birnin Jeddah na Saudiyya don lalubo martanin da za su mayar kan ƙona Ƙur’anin da Salwan Momika, ɗan asalin Iraƙi mai shekara 37, ya yi bayan ya tattaka shi a ƙofar wani masallaci a birnin Stockholm.

‘Yan sanda ne suka ba shi kariya kafin ya aiwatar da aniyar tasa, wanda ya ce ya yi hakan ne don ya nuna ‘yancinsa na faɗar albarkacin baki.

A yau Lahadi, Organization of Islamic Countries (OIC) ta shawarci ƙasashe mambobinta “su ɗauki matakin bai-ɗaya don guje wa afkuwar wulaƙanta Ƙur’ani”, kamar yadda wata sanarwa da suka fitar bayan taron ta bayyana.

“Dole ne mu ci gaba da tunasar da ƙasashen duniya game da aiwatar da dokokin ƙasa da ƙasa da gaggawa, waɗanda suka haramta nuna duk wata ƙiyayya ga addinai.”

Lamarin ya jawo zanga-zanga a faɗin duniya, inda ƙasashen Musulmi kamar Daular Larabawa da Moroko da Kuwait da Iraƙi suka kira jakadan Sweden don nuna ɓacin ransu.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp