fidelitybank

Za mu dauki matakin fansa a kan Sojoji 6 da aka kashe mana a Neja

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta yi alƙawarin ɗaukan fansa kan kisan da aka yi wa sojojinta shida bayan yi masu kwanton ɓauna yayin da suka je jihar Neja domin aikin kwantar da tarzoma.

Sojojin sun je aiki ne ƙauyen Karaga a yankin Shiroro ranar Juma’a inda wasu da rundunar ta kira ƴan ta’adda suka kai masu hari.

Wata sanarwa daga rundunar sojin ta ce an kashe da dama cikin maharan sannan kuma ana neman wasu a cikinsu.

Rundunar ta yi alƙawarin ɗaukar fansa kan kisan sojojin.

Sojojin da aka kashe sun haɗa da manyan jami’an soji biyu da wasu sojoji huɗu, a cewar rundunar. Sojoji biyu sun ji rauni a harin.

Rundunar ba ta tabbatar da rahotannin da ke cewa an yi garkuwa da wani jami’in soji.

Babu ƙarin bayani game da waɗanda suke da hannu a harin amma ana zargin ƴan bindiga da hannu a kai wa jami’an tsaro hare-hare a baya-bayan nan.

Harin ya zo ne yayin da Najeriya ke karɓar baƙuncin taron yini biyu kan yaƙi da ta’addanci a Abuja, babban birnin ƙasar.

Harin kwanton ɓaunan ya so ƴan makonni bayan kisan sojoji 16 a lokacin da suke wanzar da aikin zaman lafiya a tsakanin wasu al’umomi da ba sa ga maciji da juna a jihar Delta.

Najeriya dai na fama da matsalolin tsaro da suka shafi yin garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa da kuma ƙungiyoyin ƴan bindiga da ke kai hare-hare a sassan ƙasar sai dai hukumomi sun sha bayyana irin ƙoƙarin da suke na magance ƙalubalen da tsaron ƙasar ke fuskanta.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp