fidelitybank

Za mu dauki ma’aikata miliyan 1.4 – INEC

Date:

Hukumar zaɓe mai zaman kanta INEC, ta bayyana cewa za ta ɗauki ma’aikatan wucin-gadi kimanin miliyan 1.4.

Waɗanda suka haɗar da masu yi wa ƙasa hidima da ɗaliban manyan makarantun ƙasar da ke shekarar ƙarshe domin taimaka mata gudanar da aikin babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

Babban kwamishina a hukumar zaɓen kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da ilimantar da masu kaɗa kuri’a na hukumar Festu Okoye ne ya bayyana haka ta cikin shirin gidan Talbijin ɗin Arise TV mai suna Morning Show.

Haka kuma hukumar ta gargaɗin masu sayen ƙuri’un mutane da masu ƙirƙirar lambobin katin zaɓen da su daina aikata hakan.

Domin kuwa a cewarsa akwai bayanan kowanne kati a kan na’urarsu ta tantance masu kaɗa lkuri’a, dan haka sayen kuri’ar ba zai amfanar da su da komai ba.

Sai ma cutar da ainihin masu katunan na hana su yancinsu da kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba su na jefa kuri’a a ranar zaɓen.

Mista Okoye ya ƙara da cewa ”mun bayyana ƙarara cewa hukumarmu za ta kai na’aurar tantance masu kaɗa kuri’a a rumfunan zaɓe, domin tantance masu zaɓe, kuma bayanan kowa na ƙunshe cikin na’urar, a maimakon jikin katin zaɓen”.

”Dan haka abin da kawai jami’in zaɓe zai yi ranar zaɓe shi ne duba lambobi shidan ƙarshe da ke jikin katin zaɓenka, domin fito da bayananka daga cikin na’urar tantace masu kaɗa kuri’ar”.

”Dan haka masu sayen kuri’ar da masu kirkirar lambobin kati za su cutar da masu katunan ne kawai. Ta hanyar hana su yin zaɓe, amma dan ɗaukar katin wani domin bai wa wani ya yi amfani da shi a ranar zaɓe wannan sam ba abu ne mai yiyuwa ba”

A ranar 25 ga watan Fabairun wannan shekarar ne dai za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp