fidelitybank

Za mu dauki ma’aikata miliyan 1.4 – INEC

Date:

Hukumar zaɓe mai zaman kanta INEC, ta bayyana cewa za ta ɗauki ma’aikatan wucin-gadi kimanin miliyan 1.4.

Waɗanda suka haɗar da masu yi wa ƙasa hidima da ɗaliban manyan makarantun ƙasar da ke shekarar ƙarshe domin taimaka mata gudanar da aikin babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

Babban kwamishina a hukumar zaɓen kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da ilimantar da masu kaɗa kuri’a na hukumar Festu Okoye ne ya bayyana haka ta cikin shirin gidan Talbijin ɗin Arise TV mai suna Morning Show.

Haka kuma hukumar ta gargaɗin masu sayen ƙuri’un mutane da masu ƙirƙirar lambobin katin zaɓen da su daina aikata hakan.

Domin kuwa a cewarsa akwai bayanan kowanne kati a kan na’urarsu ta tantance masu kaɗa lkuri’a, dan haka sayen kuri’ar ba zai amfanar da su da komai ba.

Sai ma cutar da ainihin masu katunan na hana su yancinsu da kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba su na jefa kuri’a a ranar zaɓen.

Mista Okoye ya ƙara da cewa ”mun bayyana ƙarara cewa hukumarmu za ta kai na’aurar tantance masu kaɗa kuri’a a rumfunan zaɓe, domin tantance masu zaɓe, kuma bayanan kowa na ƙunshe cikin na’urar, a maimakon jikin katin zaɓen”.

”Dan haka abin da kawai jami’in zaɓe zai yi ranar zaɓe shi ne duba lambobi shidan ƙarshe da ke jikin katin zaɓenka, domin fito da bayananka daga cikin na’urar tantace masu kaɗa kuri’ar”.

”Dan haka masu sayen kuri’ar da masu kirkirar lambobin kati za su cutar da masu katunan ne kawai. Ta hanyar hana su yin zaɓe, amma dan ɗaukar katin wani domin bai wa wani ya yi amfani da shi a ranar zaɓe wannan sam ba abu ne mai yiyuwa ba”

A ranar 25 ga watan Fabairun wannan shekarar ne dai za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp