fidelitybank

Za mu dauki ma’aikata miliyan 1.4 – INEC

Date:

Hukumar zaɓe mai zaman kanta INEC, ta bayyana cewa za ta ɗauki ma’aikatan wucin-gadi kimanin miliyan 1.4.

Waɗanda suka haɗar da masu yi wa ƙasa hidima da ɗaliban manyan makarantun ƙasar da ke shekarar ƙarshe domin taimaka mata gudanar da aikin babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

Babban kwamishina a hukumar zaɓen kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da ilimantar da masu kaɗa kuri’a na hukumar Festu Okoye ne ya bayyana haka ta cikin shirin gidan Talbijin ɗin Arise TV mai suna Morning Show.

Haka kuma hukumar ta gargaɗin masu sayen ƙuri’un mutane da masu ƙirƙirar lambobin katin zaɓen da su daina aikata hakan.

Domin kuwa a cewarsa akwai bayanan kowanne kati a kan na’urarsu ta tantance masu kaɗa lkuri’a, dan haka sayen kuri’ar ba zai amfanar da su da komai ba.

Sai ma cutar da ainihin masu katunan na hana su yancinsu da kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba su na jefa kuri’a a ranar zaɓen.

Mista Okoye ya ƙara da cewa ”mun bayyana ƙarara cewa hukumarmu za ta kai na’aurar tantance masu kaɗa kuri’a a rumfunan zaɓe, domin tantance masu zaɓe, kuma bayanan kowa na ƙunshe cikin na’urar, a maimakon jikin katin zaɓen”.

”Dan haka abin da kawai jami’in zaɓe zai yi ranar zaɓe shi ne duba lambobi shidan ƙarshe da ke jikin katin zaɓenka, domin fito da bayananka daga cikin na’urar tantace masu kaɗa kuri’ar”.

”Dan haka masu sayen kuri’ar da masu kirkirar lambobin kati za su cutar da masu katunan ne kawai. Ta hanyar hana su yin zaɓe, amma dan ɗaukar katin wani domin bai wa wani ya yi amfani da shi a ranar zaɓe wannan sam ba abu ne mai yiyuwa ba”

A ranar 25 ga watan Fabairun wannan shekarar ne dai za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp