fidelitybank

Za mu dakatar da duk wasu ayyukan Hamas – Jamus

Date:

Shugaban gwamnatin Jamus, Olaf Scholz, ya ce za a dakatar da duk wasu ayyukan Hamas a Jamus, sakamakon harin da ba a taba ganin irinsa da kungiyar ta kai kan Isra’ila ba a karshen mako.

Bugu da kari, za a dakatar da kungiyar hadin kan Falasdinu ta Samidoun, in ji Scholz a wani jawabi da ya yi a gaban majalisar dokoki a Berlin a safiyar Alhamis.

Tuni dai Tarayyar Turai da Amurka ta ayyana Hamas a matsayin kungiyar ta’addanci.

Kungiyar Samidoun ta yi murna da harin da aka kai Isra’ila a ranar Asabar ta hanyar raba kayan zaki a gundumar Neukölln na Berlin.

“Wannan abin raini ne. Wannan rashin mutuntaka ne. Ya ci karo da dukkan dabi’un da muka sadaukar da su a matsayinmu na kasa,” in ji Scholz. “Ba mu yarda da kiyayya da tunzura jama’a ba tare da daukar mataki ba. Ba mu yarda da kyamar Yahudawa ba.”

Kungiyar Hamas da ke mulkin Gaza ta kaddamar da wani gagarumin harin ba-zata kan fararen hular Isra’ila a ranar Asabar.

Isra’ila ta mayar da martani da ci gaba da kai hare-hare ta sama kan yankin gabar teku mai yawan jama’a.

An kashe fiye da mutane 1,000 daga kowane bangare.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp