fidelitybank

Za mu daina kai dabbobi da kayan abinci Kudancin Najeriiya – Kungiya

Date:

Haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu fataucin dabbobi da kayan abinci ta Najeriya ta ce a shirye take ta daina safarar shanu da ma sauran kayan abinci zuwa kudancin ƙasar.

Ƙungiyar na mayar da martani ne a kan sanarwar da ƙungiyar ‘yan awaren Biafra ta IPOB ta fitar ranar Litinin, ta hana cin naman shanun da a ke shigarwa da shi daga arewacin ƙasar kama daga watan Afrilu.

A hira da BBC, shugaban ƙungiyar masu fataucin dabbobi da kayan abinci ta Najeriya Kwamared Muhammad Tahir, ya ce wannan mataki da IPOB ta dauka su ko a jikinsu.

“Muna son Najeriya ta zama kasa daya uwa daya al’umma daya, amma idan ya zamto su suna ganin hakan ta fi zame musu dai-dai to ai ta fi nono fari.” In ji Muhammad Tahir.

Ya kara da cewa ” wannan abun da ake kaiwa fa dukiya ce a ke kai musu ba tsiya ce a ke kai musu ba, abinci ne a ke kai musu ba guba ce a ke kai musu ba.”

“Saboda haka wanda ka ke kai ma wannan abinci ya ce ba ya kaunar wannan abincin sai ka ce dole ne lallai ko da yana kashe ka sai ka kai masa?”

Shugaban kungiyar masu fataucin kayan abincin daga Arewaci zuwa Kudancin Najeriyar ya jaddada cewa farfaganda ce kawai kuma “mun gaji da wannan farfaganda.

A cewarsa al’ummar Kudancin kasar ba za su iya juriyar ko da kwana daya ba a kai musu kayan abinci ko nama daga Arewacin Najeriya ba.

Dama ranar Litinin ne kungiyar da ke fafutukar ɓallewa daga Najeriya da son kafa Jamhuriyar Biafra wato IPOB, ta fitar da sanarwar haramta yin taken Najeriya da cin naman shanu da ake kai wa daga Arewa a wuraren bukukuwa da daukacin makarantun da ke Kudu maso gabashin kasar.

Kuma matakin daya ne daga cikin dokoki bakwai da IPOB ta sanar, da ta ce za ta fara aiwatar da su a 2022.

Daga ciki akwai kamfe don neman sakin fursunoninta da ake tsare da su wadanda ta ce ba su aikata wani laifi ba, da kuma batun fara zanga-zanga a manyan birane da ke fadin duniya.

Daga nan kuma ta bayyana cewa ta haramta cin naman shanu da kuma rera taken Najeriya kama daga watan Afrilun shekarar da aka shiga.

A baya yankin Kudancin Najeriyar ya fuskanci karanci da kuma tsadar kayan abinci da nama da ake shigarwa da su daga Arewacin kasar, a lokacin da kungiyar masu sayar da abincin ta shiga yajin aiki.

 

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp